Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabannin Siyasar Zimbabwe Sun Koma Teburin Shawarwari Da Nufin Ceto Shirin 'Yarjejeniyar Daunin Iko


Shugabannin siyasar Zimbabwe sun shiga yini na biyu na shawarwari da nufin ceto shirin daunin iko da aka cimma cikin watan jiya.
Tsohon shugaban Africa Ta kudu Thabo Mbeki har yanzu shi yake shiga tsakani a shawarwari tsakanin shugaba Robert Mugabe, da madugun 'yan hamayya Morgan Tsvangirai, a fadar kasar, Harare.
Ahalin yanzu kuma wani fitaccen dan siyasa Africa Wani fitaccen dan siyasa Africa Ta Kudu kuma ya fita daga Jam'iyyar ANC, wannan alamace dake ci gaba da nuna rarrabuwa a Jam'iyyar.
Mbhamzima Shilowa,tsohon Premier lardin Gauteng,ya gayawa manema labaru jiya Talata cewa zai hade da bijirarrun 'yan Jam'iyyar ANC dake shirin kafa wata sabuwar Jam'iyya. Shilowa yace bijirarrun zasu yi taron kasa na sabuwar Jam'iyyar ranar 2 ga watan gobe a wuri da za a bayyana nan gaba.
Shilowa yana cikin magoya bayan Jam'iyyar ANC da suka ajiye aiki cikin watan nan,bayanda Jam'iyyar ta tilastawa shugaban kasar Thabo Mbeki yayi murabus.
Bijirarrun suna karkashin jagorancin tsohon ministan tsaro Mosiuoa Lekota,wadda yayi zargi shugabannin Jam'iyyar da iza wutar kabilanci da kuma juyawa akidojin Demokuradiyya baya. ANC ce take mulkin kasar tun kawo karshen mulkin nuna wariya a 1994.

XS
SM
MD
LG