Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Masu Tonon Ma'adinai Sun Bukaci Gwamnatin Tarayya Tasa Ido Kan China.


Wani mai hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba.
Wani mai hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba.

Kungiyar masu tononon ma'adinai sunyi kira ga gwamnatin tarayya ta maida hankali kan sashen a zaman hanyar samun kudaden shiga.

Jigo a kungiyar masu hakar ma'adinai ta Najeriya, kuma ba sarake, Alahji Cif Husseini Abubakar yayi kira ga gwamnatin tarayya ta maida hankali kan sashen masu aikin ma'adinan, ganin cewa babbar hanyar samun kudaden shiga ga Najeriya watau man fetur sai koma baya ake samu.

Cif Husseini wanda ya zanta da wakilin Sashen Hausa Hassan Umaru Tambuwal, bayan da kungiyar ta tashi daga taron da tayi a Ibadan fadar jihar Oyo, yace ganin yadda aka sace dukiyar kasar ,akwai bukatar shugaba Buhari ya maida hankali kan wannan sashe.

Haka nan kuma Cif Husseini yayi kashedin cewa akwai matukar bukatar gwamnatin tarayya ta maida hankali kan kasar China wacce yayi zargin cewa tana kwasar ma'adinai daga Najeriya ba tareda ta biya haraji ba.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:00 0:00

XS
SM
MD
LG