A hirarsa da Abdulmugeez Idi Kotoko, Sultan Umar Faruk sarkin zangon jihar Ashanti, ya ce unguwar Ramin Kura, nan ne zangon farko da aka fara kafawa a birnin Kumasi kuma hausawa ne suka kafa zangonnin Ghana.
Sultan ya kuma bayyana cewa bambancin unguwar Ramin Kura da sauran zangonni shi ne sana'oin da ake yi a wurin, akwai mayanka, madinka, 'yan koli masu saida kayan dabbobi a wannan zangon.
Duk da cewa hausawa mazauna zangonni da yawa a Ghana an haifesu tun ma kafin a kafa Ghana, har yanzu wasu na yi musu kallon baki, wani abu da ke ci wa hausawan tuwo a kwarya a cewar Sultan. Basaraken ya kuma yi kira ga gwamnati da ta dubi wannan batu.
Saurai cikakken shirin cikin sauti.