Biyu daga cikin mutanen sun samu munanan raunuka, yayin da mutum na uku ya dan samu karamin rauni.
Dakarun na Isra’ila sun ce lamarin ya faru ne a unguwar da ake kira Adam, wacce ke tsakanin Birnin Qudus da garin Falasdinawa na Ramalla a yankin gabar Kogin Jordan.
Wannan rikici tsakanin Isra’ila da Falasdinawan, ya ta’azzara ne tun daga watan Maris, bayan da Falasdinawan suka fara bore a kullum a kan iyakar Isra’ila da zirin Gaza.
Akalla Falasdinawa 140 da kuma sojan Isra’ila daya suka mutu.
Tsageru daga yankin Gaza da ke karkashin ikon kungiyar Hamaz, sun harba rokoki zuwa yankin Yahudawa, lamarin da ya haifar da mummunan martani daga Isra’ilan
Facebook Forum