Ganin akwai gurbi a kotun kolin kasar wanda zai ba shugaba daman nada wasu alkalan kotun, Trump yace idan Clinton taci zabe, zata soke doka ta biyu dake ba Amurkawa yancin mallakar bindiga.
“Yace idan ta samu daman nada alkalan to ko baku da ta cewa. Kodayake jama’a wannan doka ta biyu kila tana nan amma ni ban sani ba”.
Bayan wasu sa’o’I sai Trump yace shi yana maganarsa ce da wata jam’iyar siyasa ce, yace babu wata fasara da za a yiwa kalaman nasa.
Amma kuwa manajan kampe na Clinton ya dauki wa’yannan kalaman Trump tamkar barazana
Manajan kampen Rooby Mook yace kalaman na Trump suna da hadari. Yace mutumin dake neman shugabancin kasar Amurka bai kamata ya rika ingiza mutane ga tashin hankali ta kowace hanya ba.