Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Fargabar Mutane Game Da Tubabbun Boko Haram


Wasu Tubabbun 'Yan Boko Haram
Wasu Tubabbun 'Yan Boko Haram

Wasu jama’a da dama sun bayyanawa wakilin Muryar Amurka Nasiru Adamu Elhikaya fargabarsu game da ragowar ‘yan boko haram da suka koma cikin daginsu da sunan tubabbu.

Wasu sun sha bayyana a wajen al'umma da sunan sun yi nadama tare da fita daga kungiyar Boko Haram, to amma a zaton wasu ma suna ganin cewa wasu sun bayyana tuban nasu ne saboda an tarwatsa su sun rasa mafaka sai su dawo gari su ce sun tuba.

Wasu daga cikin gudaddun suna komawa gaban iyayensu ne da ‘yan uwa da abokan arziki. Amma wasu jama’ar kuma suna ganin abin da yafi dacewa shine tarbiyyantar da tubabbun a ilimance ne mafita.

‘Yan Boko Haram dai sun zama babbar matsala a Najeriya, musamman ma a Arewacin kasar da ma makwabtansu. Sannan kullum hukumomin kasashen Afrika da abin ya shafa suna ta kokarin shawo kan lamarin da a mafiya yawan lokuta ake samun kwan-gaba kwan-baya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:33 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG