Gwamnatin jahar Gwambe zata gina sabbin hanyoyi 7 cikin fadar jahar. Wannan aiki zai taba gidaje da wuraren ayyukan mazauna fadar jahar.
Domin haka ne gwamnatin ta kafa kwamiti da zai kula da biyan diyya karkashin jagorancin Alahji Shehu Durbi, wanda ya gayawa Abdulwahab Mohammed, cewa bayan kwanaki uku kwamitin ya biya kashi 95 cikin dari na diyyar.
Kwamitin ya biya mutane 468 Naira Milyan 229.6, domin yadda ayyukan gina wadannan hanyoyi zata shafi ko gidajensu ko wuraren ayyukansu.
Wadansu daga cikin wadanda aikin zai shafi gidajensu suna korafin cewa diyyar da aka biya su tayi kadan. Wadansu kuma suna yaba abunda aka basu.
Ga karin bayani.