Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam'iyyun Siyasa Sun Nemi Jama'a Su Mutunta Hukuncin Kotun Koli


A Najeriya, yayin da babbar kotun koli ta kasar ta ayyana gobe Litinin a matsayin ranar da za ta yanke hukuncin kararrakin zabe na wasu gwamnonin jihohi da aka gabatar mata, a gefe guda kuma jam’iyyun siyasa sun yi kira ga magoya bayansu da su kaurace wa duk wani abun da zai kawo tashin-tashina a dangane da irin hukuncin da kotun kolin za ta bayyana.

A Jihar Bauchi, akwai shari’a tsakanin jam’iyyar PDP da kuma jam’iyyar APC wadda ta ke kalubalantar nasarar lashe zaben da jam’iyyar PDPta yi a zaben shekarar bara. A dangane da hakan jigo a jam’iyar APC ya shawarci magoya bayansu da su kasance masu bin doka da kuma umurnin kotu.

Shugaban jam’iyyar PDP a jihar Bauchi shi ma ya bukaci zaman lafiya a dangane da irin sakamakon da zai bayyana.

Gamayyar kungiyoyin farar hula ta gudanar da taro a sakatariyar ‘yan jarida a Bauchi, domin yin kira ga matasa da kuma ‘yan siyasa, dangane da muhimmancin zaman lafiya.

Saurari cikakken rahoton wakilin Muryar Amurka, Abdulwahab Muhammad.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:23 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG