Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kamaru Ta Zama Kasa Ta Farko Da Ta Shiga Zagayen 'Knockouts' A AFCON


Dan wasan Kamaru Vincent Aboubakar a lokacin da yake zura kwallo a ragar Ethiopia.
Dan wasan Kamaru Vincent Aboubakar a lokacin da yake zura kwallo a ragar Ethiopia.

Kamaru dai ta ci wasanninta biyu, inda ta doke Burkina Faso a wasanta na farko a rukuninsu na A.

Kyaftin din Kamaru Vincent Aboubakar da Karl Toko Ekambi, sun zura kwallaye biyu-biyu a ragar Ethiopia a gasar cin kofin nahiyar Afirka.

An tashi a wasan ne da ci 4-1 inda Kamarun ta lallasa kasar ta Habasha wacce ta fara zura kwallon farko a ragar Kamaru mai karbar bakuncin gasar.

Wannan nasara ta ba Kamaru damar shiga zagayen iyawarka-ta-fitar-da-kai inda za a fara sallamar kasashe zuwa gida a zangon na ‘yan 16.

Kamaru dai ta ci wasanninta biyu, inda da ta doke Burkina Faso a wasanta na farko a rukuninsu na A.

A halin da ake ciki Burkina Faso ta doke Cape Verde da 1-0 bayan kaye da ta sha a hannun masu masaukin bakin.

A ranar Juma’ar nan Gabon za ta fafata da Ghana, inda dan wasanta Pierre-Emerick Aubameyang zai dawo daga kebe kansa da ya yi.

Gwaji ya nuna Aubameyang na dauke da kwayar cutar COVID-19 yayin da suka sauka a kasar ta Kamaru a makon da ya gabata, lamarin da ya tilasta masa ya kebe kansa kamar yadda AP ya ruwaito.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG