Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Theresa May Ta Karawa 'Yan kasashen Turai Kwarin Gwiwa


Firai minsitar Birtaniya, Theresa May
Firai minsitar Birtaniya, Theresa May

Firai ministar Birtaniya Theresa May, ta yi kokarin ba miliyoyin ‘yan kasashen Turai dake zama a kasar tabbacin cewa, rayuwarsu da ta iyalansu ba za ta sauya ba, bayan da kasar ta fara shirin ficewa daga kungiyar tarayyar Turai a 2019.

Firai ministar Birtaniya Theresa May ta ce rayuwar 'yan kasashen turai da iyalansu ba za ta sauya ba duk da cewa kasar na shirin tattara inata-inata ta fice daga kungiyar tarayya ta EU, bayan da aka kada kuri'ar raba gardama a bara.

May ta yi tayin ba ‘yan asalin kasashen Kungiyar Tarayyar Turai ‘yancin zama a Birtaniyar kamar kowanne bature da aka haifa a Ingila, da wadanda aka haifa Scotland da kuma Wells, da kuma damar kula da lafiyarsu da ilimi, da tallafin marasa galihu, da kuma kudin fensho.

Za a yi amfani da dokokin kasar Birtaniya a kan al’ummomin kasashen Kungiyar ta EU, ba tare da an yi la’akkari da dokokin kotunan kasashen Turai ba.

A wani sako da ta gabatar, May ta fadawa kimanin ‘yan kasashen turai miliyan 3.1 dake zaune a Birtaniya cewa, "Muna so ku zauna."

Ta kara da cewa burinta shine ta ba dukan wadanda suke zaune a Birtaniya a halin yanzu tabbacin cewa, ba za a ce su fice daga kasar ba lokacin da Birtaniya za ta fice daga kungiyar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG