Wannan tsagaita wutar zai fara aiki ne da tsakar daren yau Lahadi. Tsagaita wutar ta biyo bayan bukatar shugaban kasar mai gudun hijira a kasar Saudiyya Abd-Rabbu Mansur Hadi.
Ya roki haka don a sami kai kayan agaji a Yamal, kamar yadda sanarwa ta fito a kafar talbijin ta Saudi Arabia. Sai dai sojojin taron dangin suna da damar maida martini matukar ‘yan Houthis ko makamantansu suka kai farmaki a lokacin tsagaita wutar.
Labarin tsagaita wutar kuma ya biyo bayan luguden wuta da aka yiwa birnin Taiz ta sama a ranar Asabar ya hallaka fararen hula kimanin 35 da jikkata da dama. Majalisar Dinkin Duniya tace rikicin watanni 4 Yamal din ya hallaka akalla mutane 3,640 rabinsu fararen hula.