Hadin gwiwar sojin Nigeria da jami’an ‘yan sandan ciki sun bayyana cewar sun gano wasu damin makamai da aka boye a wani rumbun karkashin kasa a Kebabbun unguwannin Bompai dake Arewa da birnin Kano. Jami’an tsaron suka ce sun kuma gano makaman mallakin kungiyar ‘yan gwagwarmayar Lebanon ce ta “Hezbolla”. Jami’an tsaron na Nigeria, sun nunawa manema labarai tulin makaman da suka gano jiya Alhamis, sannan daga bisani aka sake nuna tulin makaman a gidan Telbijin na Nigeria, wato NTA. Makaman sun hada harda rokokin harba makamai masu linzami da gurneti, da nakiyoyin da ake dasawa a kasa sannan a tadasu suyi barna, da kuma jigidar harsasai da bindigogin hannu.
Sojin Nigeria sun sami nasarar kame tulin makaman da aka boye a wani rumbun karkashin kasa dake jihar Kano, Nigeria
1
Ana iya gani cikin wannan hoton da rundunar sojin Nigeria ta bayar dake nuna tulin makamai iri dabam-dabam da aka gano a wani gida dake boye a Kano, Nigeria Alhamis 30 ga watan Mayun shekarar 2013.
2
Ana iya gani cikin wannan hoton da rundunar sojin Nigeria ta bayar dake nuna tulin makamai iri dabam-dabam da aka gano a wani gida dake boye a Kano, Nigeria Alhamis 30 ga watan Mayun shekarar 2013.
3
Brig. Gen. Chris Olukolade speaks to journalists from The Associated Press in an interview in Abuja, Nigeria, on Thursday, May 30, 2013.
4
Containers stocked with explosives, seized from suspected members of Hezbollah, are displayed after a raid of a building in Nigeria's northern city of Kano May 30, 2013.