A yau jumma'a da karfe 5 Sashen Hausa na Muryar Amurka tare da gidan rediyon Freedom FM dake Kano a arewacin Najeriya zasu gudanar da muhawara ta hadin guiwa kan batun bunkasa ilmi a tsakanin 'yan takarar manyan jam'iyyu a Jihar Kano.
Dukkan manyan jam'iyyun, watau ANPP mai mulki, da PDP, da CPC, da ACN sun yarda zasu turo wadanda za su bayyana shirye-shiryensu na bunkasa ilmi a Jihar idan har aka zabe su.
Masu sauraro zasu iya shiga cikin wannan muhawara ta hanyar bayyana a dakin shirye-shirye na gidan Rediyon Freedom a Kano, ko kuma ta kira kai tsaye zuwa nan Washington a kan wadannan lambobi:
+12026190154 ko kuma +12026190155
Wannan muhawara dai zata ta'allaka ne kan hanyoyin magance matsalolin da suke fuskantar ilmi, musamman a jihar Kano da kuma jihohin arewacin Najeriya inda aka samu koma-baya sosai cikin 'yan shekarun nan a fagen ilmi.