Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotun Shari'ar Musulunci Ta Yankewa Wasu Mutum 3 Hukunci Kan Yin Luwadi


NIGERIA-ISLAM-COURT-charia
NIGERIA-ISLAM-COURT-charia

Wata kotun shari’ar Musulunci a jihar Bauchi da ke arewacin Najeriya ta yanke wa wasu mutane uku hukuncin kisa ta hanyar jifa, bayan ta same su da laifin yin luwadi, kamar yadda shugaban ‘yan Hisban da ya kama su a ranar Juma’a ya bayyana.

Arewacin Najeriya galibi musulmi ne kuma jihohin da ke yankin na amfani da kotunan shari’a wajen hukunta mutanen da suka aikata laifukan da suka hada da zina da wani sabo.

Adam Dan Kafi, shugaban Hisbah na karamar hukumar Ningi da ke Bauchi ya ce an kama mutanen uku ne a ranar 14 ga watan Yuni, kuma aka gurfanar da su a gaban kotun shari’a.

Mutanen da suka hada da wani tsoho mai shekaru 70, duk sun amsa laifinsu duk da cewa ba lauyoyi ne suka tsaya musu ba, in ji Kafi.

Ya ce mai shari’a Munka’ilu Sabo ya yanke musu hukuncin kisa ne a ranar Alhamis, amma za su iya daukaka kara kan hukuncin nan da kwanaki 30.

Duk wani hukuncin kisa da kotunan shari’ar Musulunci za ta zartar a Najeriya na bukatar amincewar gwamnan jihar.

A Najeriya, kamar yawancin sassan Afirka, ana kallon luwadi a matsayin abin da ba za a amince da shi ba.

Najeriya wadda ita ce kasa mafi yawan al'umma a nahiyar Afirka, tana da wata doka da ta ba da damar dauri a gidan yari ga wadanda aka samu da laifin nuna jinsi daya a bainar jama'a da kuma masu auren jinsi daya.

Hukuncin da aka yanke a Bauchi zai kuma iya haskawa a kan matsayin shari’ar Musulunci a kasar da tsarin mulkinta ya yi watsi da addini.

A watan da ya gabata ne wani mawakin Najeriya ya bukaci kotun daukaka kara da ta bayyana hukuncin shari'a a wata jihar da ta sabawa kundin tsarin mulkin kasar. Ana sa ran yanke hukunci kafin Oktoba.

XS
SM
MD
LG