#ENDSARS: Zanga Zangar Kyamar Gallazawa Al’umma Da Yan Sanda Ke Yi
Wannan sashi na musamman ya hada da rahotanni Sashen Hausa na Muryar Amurka kan zanga zangar kin jinin rundunar ‘yan sanda ta musaman mai yaki da fashi da makami (SARS), da aka fara a farkon watan Oktoba 2020. Nan da nan zanga- zangar ta zama wani gagarumin gangamin adawa da gasawa al’umma akuba da ‘yan sanda ke yi a Najeriya. Zanga –Zangar da aka ba lakabi da #ENDSARS ta yi kira da a rushe rundunar ‘yan sanda ta musaman mai yaki da fashi da makami (SARS), wata rundunar ‘yan sanda da ta yi kaurin suna wajen gasawa al’umma aya a hannu.