Yayin da al'amura ke cigaba da tabarbarewa a Janhuriyar Afirka Ta Tsakiya, duk kuwa da gudanar da zabe cikin nasara a watan Janairun da ya gabata, an hallaka wasu sojojin Majalisar Dinkin Duniya biyu, al'amarin da ya sa Majalisar ta dinkin duniya ta koka.