Asabar yayi murabus bayan ya gabatar a wani jawabi na sukar lamirin Hezbollah da Iran.
Rera taken a wajen biki, zai sa a daure mutum kwanaki 15 a gidan yari.
A karon farko tun bayan mummunan matakin soji da aka dauka a kan Musulmi ‘yan kabilar Rohingya, jagorar kasar Myanmar, Aung Suu Kyi, ta kai ziyara jihar Rakhine mai fama da rikicin da ke faruwa a arewacin kasar.
A yayinda rundunar hadin guiwar kasashen da ake kira G5 Sahel ta kaddamar da ayyukan sintiri a fagen fama, hukumomin janhuriyar Niger sun bukaci kasar Amurka ta fara amfani da jirage masu sarrafa kansu domin fatattakar ‘yan ta’adda akan iyakar kasar da Mali.
Ranar biyu ga watan Nuwamba rana ce ta musamman da Majalissar Dinkin Duniya ta ware don yin nazari aka yadda ake kuntatawa ‘yan jarida.
Kakakin shugabar kasar Myanmar ya shaidawa manema labarai cewa kasar Bangladesh na jiran karbar dalar Amurka miliyan dari hudu ne, kafin ta bar 'yan Rohingya 600,000 da yanzu suke makale a karamin wuri wucewa shiga kasarta
Rikicin Yemen ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 10,000 ya kuma haddasa matsalar taimakon jinkai.
Kudin agajin jinkai da Bangladesh ta samu daga kasashe na iya kawo tsaiko a shirin maida 'yan Rohingya kasarsu a cewar gwamnatin Myanmar.
Kwana kwanan nan aka kwato birnin Raqqa daga hannun mayakan ISIS amma akwai dubban nakiyoyi da aka binne saboda haka hadari ne mutane su koma birnin yanzu, sai su dakata har sai an kakkabe bama baman.
Kungiyar ISIS ta dauki alhakin harin kunar bakin waken da aka kai a unguwar jakadun kasashen waje a Kabul babban birnin kasar Afghanistan, harin ya yi sanadiyar mutuwar mutane takwas kuma an aunashi ne kan yankin dake kusa da ofishin jakadancin Amurka
Domin Kari