A wani al'amari na ba-zata, Shugaban kasar Iran Hassan Ruhani ya amsa cewa mutanen kasar na da izinin bayyana bacin ransa game da manufofin gwamnatin kasar ta hanyar zanga-zanga. Kalaman na Ruhani, da ake ganin wata hanya ce ta rarrashi da kuma iya tattalin hankalin wanda ake mulka idan ya fusata, ya yi ne a jawabinsa ga Majalisar Ministocinsa.