Birtaniya na shirin daukan matakin kan Iran saboda kwace mata jirgin dakon manta da ta yi a Mashigin Hormuz.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce halin da ake ciki a Siriya na dada kazancewa, kuma miliyoyin mutane na ci gaba da fama da karancin kayan jinkai a fadin kasar.
Ana sa ran jam'iyyar sabon shugaban kasar ta taka rawar gani a wannan zabi, inda akasin hakan zai tilasta mata kafa gwamnatin hadaka.
Hukumomin tsaron ruwan Iran sun ba da umurnin a kama jirgin ruwan na Birtaniya mai suna Stena Impero, saboda a cewarsu, “bai bi ka’idojin safara akan tekun ba.”
Adadin ‘yan jarida da aka kashe a kan aikinsu a shekarar 2018, ya ninka abin da aka gani a shekarar 2017 a cewar wata kungiya mai zaman kanta a nan Amurka ta Committee to Protect Journalists.
Hukumomin Pakistan sun ce an kama Hafiz Saeed a yau Laraba a mahaifarsa da ke Lardin Punjab a kusa da wani gari da ake kira Gujranwala.
Kasar Iran ta yi barazanar farfado da shirinta na nukiliya zuwa matakin da ya ke kafin ta rattaba hannu a yarjajjeniyar 2015 da manyan kasashen duniya shida.
Domin Kari