Jiya Alhamis, magadan gari sama da 200 a Amurka, sun bukaci ‘yan majalisar dattawa da su dawo daga hutun lokacin barazar "Summer", su rattaba hannu kan kudurin dokar dakile wanzuwar bindigogi.
Shugaban Donald Trump ya kai ziyara tare da mai dakinsa, don jinjinawa wadanda suka fara kai daukin farko da kuma tattunawa tare da iyalai da suke zaman makoki da wadanda suka tsira daga wannan bala’in.
Ofishin babban hafsan sojan Koera ta Kudu ya ce Korea ta Arewa tas Arewa sake ta cilla wadanan makaman masu linzami masu cin matsakaicin zango guda biyu, zuwa yammacin kasar ne.
Da ya ke mai da martani kan hare-haren kan mai uwa da wabin nan da aka kai a Amurka, Shugaban Amurkar Donald Trump ya sha alwashin, abin da ya kira, daukar matakin gaggawa.
Donald Trump ya bukaci a sauke tutocin kasar a gine-ginan gwamnati har na tsawon kwanaki biyar masu zuwa yayin nuna alhini.
A wani zub da jini na tsawon sa’o’I 13 a Amurka, wasu mahara biyu a wurare daban daban, sun kashe mutane 29 kana suka jikata wasu da dama, yayin da hukumomi ke binciken musabbabin wadannan munanan hare hare.
Wannan hari na baya-bayan nan, na zuwa ne ‘yan sa’o’i bayan wani harin kan-mai-uwa-da-wabi, da aka kai a garin El paso da ke jihar Texas, a kantin sayar da kayayyaki na Walmart, inda mutum 20 suka mutu kana wasu 26 suka jikkata.
Kakakin ‘yan sandan yankin, Sergeant Enrique Carrillo, ya ce an kama wani mutum da ake zargi da kai harin.
Ana sa ran takunkumin zai fara aiki kwanaki 15 bayan an sanar da majalisar dokokin kasar kan wannan mataki, wanda zai kai tsawon shekara guda.
Bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar Mallaka da Amfani da makaman nukiliya masu cin matsakai cin zango, shugaban Donald Trump, ya ce yana fatan nan gaba za’a kulla wata sabuwar yarjejeniyar da zata maye wannan da ta wargaje a yanzu.
Wannan mataki ne da ba a saba gani ba da Trump ya dauka, akan Ministan Harkokin Wajen Iran, Mohammed Javad Zarif.
Domin Kari