WASHINGTON, D.C - A yau Alhamis ne Kalonzo Musyoka yake magana da manema labarai a birnin Nairobi, a daidai lokacinda ake ci gaba da kirga kuri’un da hannu bayanda na’urorin komputa da ake amfani da su, suka ja suka tsaya.
I zuwa safiyar yau Alhamis dai an kirga kuri’u kusan rabin milyan kuma sakamakon na nuna cewa Uhuru Kenyatta na da kashi 53% na kuri’un yayinda abokin takarar nashi Raila Odinga ke da kashi 42%.
I zuwa safiyar yau Alhamis dai an kirga kuri’u kusan rabin milyan kuma sakamakon na nuna cewa Uhuru Kenyatta na da kashi 53% na kuri’un yayinda abokin takarar nashi Raila Odinga ke da kashi 42%.