Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsohon Madugun 'Yan Tawayen Hutu Na Burundi Ya Ajiye Mukaminsa


Tsohon madugun 'yan tawayen kabilar Hutu na kasar Burundi, Pierre Nkurunziza, ya ayyana ajiye mukaminsa na madugun 'yan tawaye a yayin da yake shirin zamowa shugaban kasar.

A jiya jumma'a Mr. Nkurunziza tare da wasu tsoffin mayaka 40 suka mika makamansu a wurin wani bukin da aka shirya na kwance damarar yaki a Muramuya.

Tsohon maduhgun 'yan tawayen, wanda yake jagorancin kungiyar nan mai suna "Dakarun Kare Dimokuradiyya" ko FDD a takaice, shi kadai yake takara a zaben shugaban kasar Burundi da za a yi ranar 19 ga watan nan na Agusta.

FDD ta doke dukkan abokan adawar siyasarta a zabubbuka na yankuna da na kasa baki daya da aka yi cikin watannin Yuni da Yuli, ta samu gagarumin rinjaye a majalisun dokoki na tarayya, matakin da ya sa babu wanda zai iya zama shugaban kasa sai shi Mr. Nkurunziza.

An kashe mutanen da yawansu ya kai zambar 300 a yakin basasar shekaru 12 a kasar Burundi, wanda a yanzu wata kungiya kwaya daya tak ta 'yan kabilar Hutu ce mai suna national Liberation Forces take gudanar da shi. Wannan yaki na Burundi ya barke a bayan da sojojin kasar wadanda 'yan kabilar Tutsi 'yan tsiraru suka kanainaye, suka kashe shugaban kasar dan kabilar Hutu wanda aka zaba ta hanyar dimokuradiyya.

XS
SM
MD
LG