Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nigeria ta bada sanarwar ranakkun da za’a gudanarda zabukkan shugaban kasa


Hukumar zaben Nigeria ta bada sanarwar ranakkun da za’a gudanarda zabukkan shugaban kasa, gwamnoni da yankunan kananan hukumomi. Hukumar zaben tace a ran 21 ga watan Afrilun badi ne za’a gudanarda zaben shugaban kasa da na ‘yanmajalisun tarayya, amma zaben gwamnoni da na majalisun jihohi ne za’a fara yi a ran 14 ga watan na Afrilu. Shugaban hukumar zaben Maurice Iwu yace anyi tanadin gudanarda zabukkan raba gardama a cikin lokaci ta yadda za’a tabattarda cewa an rantsarda sabuwar gwamnati a ran 29 ga watan Mayu na badi. A cikin wannan watan na Mayu na badin ne shugaban Nigeria na yanzu Olusegun Obasanjo zai kamalla wa’adodinsa guda biyu. A farkon shekaran nan ne dai majalisun tarayya na Nigeria suka kashe yunkurin da akso yi na chanja kundin tsarin mulki don baiwa shugaba Obasanjo damar yin wa’adi na ukku.
XS
SM
MD
LG