Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Bukaci China Ta Daina Garkame Musulmi Kabilar Uighur


Jami'an tsaron China a harabar wani masallacin Uighur da ke yammacin China
Jami'an tsaron China a harabar wani masallacin Uighur da ke yammacin China

Garkame al'ummar musulmi musamman 'yan kabilar Uighur da sauran tsirarun al'ummomin musulmai da China ta ke yi a wasu sansanoni, ya ja hankalin Amurka, wadda ta yi tir da hakan, tare da kiran China ta daina.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Mike Pompeo, ya bayyana garkame al’ummar Musulmi, akasari ‘yan kabilar Uighur, da sauran tsirarun al’ummomi Musulmi, da kasar China ta yi a wasu sansanonin da ke yankin Xinjiang na yammacin kasar, da cewa abin tayar da hankali ne kuma na yin Allah wadai.

“Mun sha fitowa fili mu na yin tir da hakan, kuma mun yi ta tattaunawa da China a kebance kan wannan batu,” a cewar Pompeo yayin da ya ke amsa tambayar da Muryar Amurka ta masa kan batun.

Ya kara da cewa Amurka na kan kokarin shawo kan China ta gane cewa hakan bai dace ba, kuma ta daina.

Dama kungiyoyin kare hakkin dan adam sun zargi kasar ta China da garkame miliyoyin ‘yan kabilar Uighurs.

A martaninta, China ta ce shirin kawar da tsaurin ra’ayi ta ke yi, kuma ana koyar da ayyukan yi da doka da kuma harshen Sin na Mandarin a sansanonin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG