Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Bude Iyakar Kamaru Da Najeriya Domin Gudanar Da Kasuwanci


Commercent d'Odontole a Abong-Mbang, Cameroun, le 21 novembre 2016. (VOA/Moki Edwin Kindzeka)
Commercent d'Odontole a Abong-Mbang, Cameroun, le 21 novembre 2016. (VOA/Moki Edwin Kindzeka)

A cikin tsanaki da taka tsan-tsan kasar kamaru ta bude iyakarta da Najeriya, inda ta fara gudanar da kasuwanci, shekaru 3 bayan da ta rufe iyakar sakamakon rikicin ‘yan Boko Haram.

Kasar dake yankin tsakiyar Afrika ta ce kodayake an sake bude hada-hadar kasuwanci da Najeriya saboda saukin hare-haren ‘yan boko haram da aka samu cikin shekaru 2 da suka gabata, duk dan kasuwar da zai je Najeriya ya koma kasar dole ne sai anyi mai binciken kwakwaf.

Daruruwan ‘yan kasuwa sun koma kasuwar Lami dake kan iyaka a yankin jihar arewa mai nisa dake kasar kamaru. Sun cigaba da saye da sayarwa da takwarorinsu daga Najeriya.

Sakatare-Janar din kasuwar Gambari Ngara na Najeriya, Alhaji Bakari Balje, yace sun yanke shawarar sake bude iyakar ne saboda hare-haren ‘yan boko haram sun yi sauki kuma akwai bukatar cigaba da hada-hadar kasuwanci tsakanin Najeriya da Kamaru.

Mijinyawa Bakari, gwamnan jihar arewa mai nisa, ya ce matsanancin talauci da kuncin rayuwa a yankin da mafi akansin jama’ar ‘yan kasuwa ne da manoma, zai ragu. Amma yace za a asa ido akan jama’a da sana'o'insu.

XS
SM
MD
LG