Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An kai sabon hari a kauyen Rukubi jihar Nasarawa har an kashe mutane goma sha shida


Gawar mutane da aka kashe lokacin rikici
Gawar mutane da aka kashe lokacin rikici
Kimanin wajen mutane goma sha shida a kashe a kauyen Rukubi cikin karamar hukumar Doma a jihar Nasarawa. Jiya da safe yayin da mutane suka tashi wasu na shirin zuwa aiki wasu kuma na kokarin zuwa gonakansu sai kwaram wasu da bindigoji suka farma kauyen suna harbi. Sun kashe mutane goma sha shida nan take sun kuma kone gidaje wajen ashirin.

Wani ganao ya ce ya kirga gawarwaki goma sha shida a cikin kauyen ban da na bayan gari. Wasu da aka zanta da su sun ce basu san komai ba sai suka fara jin harbe-harbe da safe. Ta dalilin haka ya sa sauran jama'a suka fantsama cikin daji domin su ceci rayukansu.

Kawo lokacin rahoton nan jami'an tsaro basu da masaniya kan lamarin kamar yadda Zainab Babaji ta bayyana a rahotonta.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:44 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG