Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sami Mutum 6 Da Cutar Coronavirus A Taraba


Alkaluman yaduwar kwayar cutar coronavirus na Kara karuwa a wasu jihohin Najeriya, inda wasu jihohin da ada ba'a samu bullar cutar ba, yanzu sun sami sababbin kamuwa da cutar.

Jihar Taraba ta samu mutum shida da suka kamu kamar yadda alkalumma hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa ta Najeriya NCDC ta bayyana.

karin alkaluman na zuwa ne a dai dai lokacin da gwamnatocin jihohin suka kafa dokar hana shiga jihohinsu da kuma dokar zama a gida, batun da wasu ke ganin akwai abin dubawa.

Mallam Abdullahi Tukur wani mai fashin baki ya ce, muddin gwamnati bata taimaka wajen samar da abinci ga jama'a ba, to da wuya irin wadannan dokoki su yi tasiri.

Saurari Karin cikin sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:50 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG