WASHINGTON, DC —
Wakilin Sashen Hausa a Kaduna, Iliya Kure, ya aiko da rahoton cewa shugaban Hukumar aikin Ziyarar Ibadar Kiristocin Najeriya Mr. John Kennedy Okpara ya ce an yiwa Kiristocin Najeriya rangwamen kashi goma sha biyu cikin dari daga kudaden da za su biya su je aikin ziyarar ibada a Israila da Girka da kuma birnin Roma.
Rangwamen ya samu ne bayan amincewar da shugaba Jonathan ya yi a sayar da dolar Amurka daya akan Naira 146 a maimakon 160 din da aka saba