Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Babu Dalilin Kama Omar Al-Bashir A Najeriya: Hassan Tukur


Shugabannin kasashen cikin kungiyar Tarayyar Afirka a wurin taron
Shugabannin kasashen cikin kungiyar Tarayyar Afirka a wurin taron

Ambasada Hassan Tukur, babban jami'i a ofishin shugaban Najeriya yace shugaban kasar Sudan Omar Al-Bashir yaje Najeriya ne bisa gayyatar Kungiyar hadin kan Afrika

A daidai lokacin da shugabannin kasashen nahiyar Afrika ke halartar wani kasaitaccen taro a babban birnin tarayya Abuja, da zumar yaki da cututukan tarin fuka da kamjamau da kuma zazazabin cizon sauro, hankalin wadansu ‘yan gwaggwarmaya ya koma kan batun sammacen da kotun duniya ta bayar na kama shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir.

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Right Watch da kuma wata kungiya mai suna Kungiyar kawancen masu goyon bayan kutun duniya ta Najeriya, sun garzaya kotu domin neman ta tilastawa gwamnatin tarayya umarta kama shugaba Omar Al-bashir.

A cikin hirarsu da wakilinmu Umar Faruk Musa, wani babban jami’i a ofishin shugaban kasa, jakade Hassan Tukur ya bayyana cewa, shugaban kasar Mali yaje Najeriya ne bisa gayyata da kuma amincewar kungiyar hadin kan Afirka wadda ta goyi bayan wofinta sammacen na kotun duniya, sabili da haka babu dalilin da zai sa Najeriya ta bada umarnin kama shi.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:10 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG