Hukumomin Nijar sun ce daga cikin wadanda suka mutu har da sojojin Najeriya biyu.
Wadanda suka shaida lamarin sun gayawa Muryar Amurka cewa baya ga harin da suka kai a sansanin sojin 'yan kungiyar ta Boko Haram sun kuma kona barikin baki daya.
"Muna shiga sai muka ga mutanen da aka karkashe kawai ba mu tsaya ba sai muka fita." Inji wani mazaunin yankin garin na Boso da ya nemi kada a ambaci sunansa.
Jamhuriyar Nijar da ke makwabtaka da Najeriya ita ma ta shiga fama da matsalar tsaro tun bayan da 'yan kungiyar ta Boko Haram suka fara kai hare-hare a yankin tafkin Chadi.
Domin jin cikakken bayani kan wannan hari saurari hirar da wakiliyar Muryar Amurka Tamar Abari ta yi da wani mazaunin yankin da kuma rahoton da Sule Mumuni Barma ya aiko mana: