Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

LIBYA: Firayim Ministan Ya Yadda Ya Yi Murabus


Wakilin Libya Ashour Abu-Rashed a taron neman sulhu
Wakilin Libya Ashour Abu-Rashed a taron neman sulhu

Prime ministan kasar Libya da duniya ta amince dashi ya fada jiya talata cewa zaiyi murabus muddin hakan shine bukatar jamaar kasar.

Sailin da yake Geneva, Manzon Libya na musammam a Majalisar Dinkin Duniya ya bukaci bangarorin biyu masu fada da juna su amince domin a samar da gwamnatin hadin gwiwa.

Prime Ministan Abdullahi al-Thani ya sha suka mai tsananin gaske, a sailin da ake hira dashi a gidan talabijin , inda masu kallo ke cewa gwamnatin bata tabuka komai,Sai dai yace yace a shirye yake da ya yimurabus muddin wannan shine abinda jamaar kasar keso.

Mai Magana da yawun gwamnatin ya shaidawa kanfanin dillacin labarai na Reuters cewa kalaman na Prime Ministan ba sanarwa ce a hukunce ba cewa ya sauka daga mukamin nasa.

Gwamnati kasar Libya dai ta kasu gida biyu, daya tana Gabashin birnin Tobruk, sai kuma wadda keda goyomn bayan masu tsananin raayin addini dake cikin birnin Tripol

XS
SM
MD
LG