Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Masu Son Faransa Ta Kwashe Dakarunta A Nijar Sun Yi Gangami A Yamai


Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar
Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar

Wasu 'yan Nijar na ganin Faransa ba ta tabuka wani abin a-zo-a-gani a yakin da take yi da ayyukan ta'addanci a kasar da ma yankin Sahel baki daya.

NIAMEY, NIGER - Daruruwan mazauna birnin Yamai sun yi dandazo a yammacin Juma'a a kofar sansanin sojin Faransa da ke filin jirgin sama na Escadrille da nufin nuna bukatar Faransa ta kwashe dakarun da ta girke a Nijar da sunan yaki da ta'addanci.

Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar
Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar

Faransa na da sojojin sama da 1,000 jibge a kasar ta Nijar, wacce ke fama da rikicin shugabanci sanadiyyar juyin mulki da sojoji suka yi.

Wannan shi ne karon farko da 'yan Nijar ke samun damar yin dandazo a sansanin sojan na Faransa duk da ya ke an shafe shekaru suna nuna bukatar ficewar sojojin daga kasar.

Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar
Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar

Wasu 'yan kasar na ganin cewa Faransa ba ta tabuka wani abin a-zo-a-gani a yaki da ayyukan ta'addanci a Nijar da yankin Sahel baki daya.

Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar
Daruruwan ‘Yan Nijar Sun Taru Suna Bukatar Faransa Ta Kwashe Dakarun Ta Daga kasar

A halin yanzu dai dangantaka na kara dagulewa ne a tsakanin Faransa da hukumomin Nijar tun bayan juyin mulkin da ya hambarar da zababben Shugaban kasar Mohamed Bazoum a ranar 26 ga watan Yuli.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG