Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nan Ba Dadewa Ba Za'a Murkushe Kungiyar ISIS - Shugaban Faransa


Shugaban Faransa yayinda ya kai ziyara Iraqi
Shugaban Faransa yayinda ya kai ziyara Iraqi

Shugaban Faransa Francosi Hollande, yayi alwashin cewa nan bada jumawa ba za'a sami galaba kan kungiyar ISIS. Holland yayi wanan furucin ne lokacinda ya kai ziyarar wuni daya a a Iraqi,a ranar kuma wani dan kunar bakin wake ya kai kari a wata kasuwa a Bagadaza, ya halaka mutane 32.

"Deash tana tsamurewa.Kuma za'a yi galaba akanta," inji Holland, ya kira kungiyar da lakabin da ake kiranta da labaraci.

Sa'o'i bayanda Holland isa Iraqi a jiya Litinin, bam ya tashi a wata kasuwa dake unguwar Sadr dake gabashin birnin dake shake da leburori. Kungiyar ISIS ta dauki alhakin kai harin.

A lokacin da suka yi taro da menama labarai tareda shugaban na Faransa, PM Iraqi Haider al-Abadi, yace maharin ya shigo kasuwar a zaman wand a yake son ya dauki lebori aiki, daga nan ne ya tada bam din.

Haka nan Holland ya gana da shugaban kasar na Iraqi na jeka na-yi ka Fuad Masum, daga bisani ya ziyarci yankin arewacin kasar na kurdawa mai kwariya-kwariyar cin gashin kai har ya gana d a shugabannin yankin.

Shugaban na Faransa ya kuma ziyarci sojopjin kasarsa a Bagadaza, da kuma wadanda suke yankin Kurdistan wadanda suke taimakawa a fafatawar da da ake yi d a 'yan kungiyar ISIS., ya gayawa dakarun cewa kokarinsu yana taimakawa wajen hana akai musu hare-haren ta'addanci a can kjasarsu.

XS
SM
MD
LG