Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijar Ta Jinkirta Zabe Na Wasu 'Yan Kwanaki


Janar Salou Djibo, shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar yana jefa kuri'arsa lokacin da aka kada kuri'ar amincewa da sabon tsarin mulki, ranar 31 Oktoba, 2010
Janar Salou Djibo, shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar yana jefa kuri'arsa lokacin da aka kada kuri'ar amincewa da sabon tsarin mulki, ranar 31 Oktoba, 2010

Matsalolin kayan aiki sun sa na jinkirta zabubbukan majalisun birane da yankunan kananan hukumomi har sai ranar talata

Jami'an zabe a Jamhuriyar Nijar sun jinkirta zabubbukan majalisun birane da kananan hukumomi na tsawon kwanaki uku a saboda matsalolin kayan aiki.

A yanzu an shirya gudanar da wadannan zabubbukan a ranar talata, maimakon ranar asabar kamar yadda aka tsara tun da fari.

Shugaban hukumar zaben Nijar, Ghousmane Abdourahmane, ya fadawa 'yan jarida jiya alhamis cewa wasu rumfunan zabe ba su samu takardun kuri'a da wasu kayayyakin zaben ba.

Zabubbukan su ne mataki na gaba da aka tsara da nufin mayarda kasar dake Afirka ta Yamma kan turbar mulkin dimokuradiyya ta farar hula.

A watan Fabrairu ne sojoji suka hambarar da shugaba Mamadou Tandja daga kan mulki a bayan da ya sauya tsarin mulkin kasar domin kara wa'adin zamansa a kan karagar mulki.

A watan Oktoba, masu jefa kuri'a sun amince da sabon tsarin mulki wanda ya ba sojoji wa'adin zuwa ranar 6 ga watan Afrilu domin su maido da mulkin farar hula.

Kasar ta shirya gudanar da zaben shugaban kasa a ranar 31 ga watan nan na janairu.

XS
SM
MD
LG