Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

PDP Na Daukar Matakan Kwace Madafun Iko A Najeriya


Sanata Ali Modu Sheriff
Sanata Ali Modu Sheriff

Yayin da gwamnatin Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ke cika shekara guda a watan mayu na gobe, Jam’iyyar Hamayya ta PDP tana daukar matakan kwace madafun iko a shekara ta 2019. Hakan dai na daga cikin kalaman shugaban PDP na kasa Sanata Ali Modu Sheriff lokacin daya ke jawabi ga ‘yayan Jam’iyyar jiya a Dutse jihar Jiagwa.

Shugaban wanda ya fara da jihar Jigawa a jadawalin kewaya jahohin Najeriya da ya tsara, domin ganawa da magoya baya gabanin taron kolin jam’iyyar ta PDP da za a yi a watan gobe, yace hakan na daga cikin alkawarinsa na farfado da ruhin jam’iyyar.

Shi kuma tsohon gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido, dake zaman babban mai masaukin baki ya yi jawabi a taron inda ya furta kalaman da ke koda sabon shugaban Jam’iyyar Ali Modu, yayi kuma fatan sake karbar ikon jihar a zaben shekara ta 2019.

Dangane da tsarin yar tinke da PDP tace zatayi amfani da shi wajen fitar da yan takara a zaben 2019, Ambasada Kazaure yace, yin hakan zai nunawa Najeriya cewa Dimokaradiyya ta nuna a wajen yan PDP, haka kuma za a gudanar da hakan ba tare da samun tangarda ba, harma da zaben wanda jama’a ke so.

Saurari rahotan don karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00

XS
SM
MD
LG