Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sabon Babban Sakataren MDD Zai Ba Matakan Rigakafin Aukuwar Rikici Fifiko


Sabon Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ko MDD, Antonio Guterres.
Sabon Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ko MDD, Antonio Guterres.

Sabon baban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Gueterres, wanda yace rigakafin aukuwar rikice rikice zai baiwa fifiko. Jiya Talata ya gabatar da bayanin abinda yake begen ganin Majalisar Dinkin Duniya, ko MDD tayi daga maida martini ko kuma kai doki bayan aukuwar rikici zuwa ga rigakafin aukuwar su.

Antonio Gueteres yace maida martini bayan rikici ya auku ya kanainaiya aikin Majalisar Dinkin Duniya shekara da shekaru. Yace lokaci yayi daya kamata Majalisar ta dauki matakan rigakafin barkewar rikici domin tabbatar da zaman lafiya.

Mr Gueterres yace tilas rigakafi ya zama abinda za’a rika yi a kowane lokaci. Muhimmin mataki ne na rage wahala da jama’a suke sha domin cimma burorinsu ta rayuwa.

Haka kuma sabon sakataren na Majalisar Dinkin Duniya yayi kira ga kasashen duniya da su maida hankali wajen amfani da dabarun diplomasiya domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.

XS
SM
MD
LG