Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sudan Ta Kudu Na Fuskantar Kalubalen Kayan Agaji


Mataimakin Shugaban Sudan ta Kudu na 'daya Taban Deng Gai
Mataimakin Shugaban Sudan ta Kudu na 'daya Taban Deng Gai

Mataimakin shagaban Sudan ta Kudu na farko, Taban Deng Gai yana kira ga kasashen duniya masu taimako da kada su yi watsi da kasar tashi a daidan wannan lakoci da da kasar ke cikin mawuyacin hali, na yawan yake-yake.

Haka kuma wannan sabuwar kasa ta duniya na huskantar kalubalolin kayan agaji, a yayin da dubban yan kasar suka gudu, suka yi hijira zuwa kasashen dake makwaptaka da ita don neman mafaka.

Deng ya fada jiya Alhamis a wurin taron MDD a New York, cewa halin da al’ummar kasar ke ciki na wahala ya wuce gona da iri.

Mataimakin shugaban na Sudan ta Kudu Deng ya kara da cewar yake-yake a wannan shekara a yankunan Wau, da Raja, da kuma Juba sun kara dagula al’amura.

Sai dai kuma ya dora laifi a kan ambaliyar da aka samu sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya wadda ta fid da mutane daga gidajensu a jihohin Upper Nile da kuma Bahr al Ghazal.

Duk da wannan hali da ake ciki, Deng yace hankali ya soma kwantawa a kasar ta Sudan ta Kudu.

An dai yi wani zaman tattaunawa a jiya Alhamis a wurin taron MDD a kan rikicin Suda ta Kudu da kuma kalubalolin da take fuskanta na kayan agaji.

XS
SM
MD
LG