Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tattauna Hanyoyin Yaki da Talauci a Najeriya a Taron Kasa Zai fi Amfani


Nigeria National Assembly
Nigeria National Assembly

Kungiyar hada kan arewacin Najeriya tace tattauna hanyoyin yaki da talauci a Najeriya a taron kasa zai fi amfani

Kungiyar hada kan matasan arewacin Najeriya tace tattauna hanyoyin yaki da talauci a Najeriya, a taron kasa zai fi amfani ga al'umar Najeriya.

Shugaban, kungiyar Hassan Waziri Chinade ne ya furta haka a wata hira da yayi da wakilin Muryar Amurka, Nasiru Adamu El-Hikaya.

Yace yankin arewacin Najeriya, yafi sauran yankunan kasar yawan matasa, masu karancin ilimi da kuma karin talauci.

Wanda a cewarsa baida alfanu ga kasar, domin rashin ilimi da kuma talauci shike sa matasa fadawa aikata abubuwan da basu dace ba.

A wani labarin kuma Igwe Martins na yankin Ibo yayi watsi da masu dawo da kamfe din raba kasa ko kuma kafa kasar Biafra.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:29 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG