Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Turkiyya Ta Bi Sahun Afirka Ta Kudu Wajen Shigar Da Karar Isra’ila A Kotun Duniya Kan Kisan Kare Dangi


Shugaban kasar Türkiye Recep Tayyip Erdogan, Baghdad, Iraq, Afrilu 22, 2024.
Shugaban kasar Türkiye Recep Tayyip Erdogan, Baghdad, Iraq, Afrilu 22, 2024.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya bayyana a ranar Laraba cewa, Turkiyya za ta bi sahun Afirka ta Kudu wajen shigar da kara kan kisan kiyashin da Isra'ila ke yi a kotun kasa da kasa (ICJ).

WASHINGTON, D. C. - Fidan ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da ministan harkokin wajen Indonesia Retno Marsudi a Ankara babban birnin kasar Turkiyya, inda ya ce "Bayan kammala rubutun aikinmu na doka, za mu gabatar da sanarwar shiga tsakani a hukumance a gaban kotun ICJ da nufin aiwatar da wannan shawarar ta siyasa."

"Turkiyya za ta ci gaba da tallafa wa al'ummar Palasdinu a kowane hali," in ji shi.

Kotun ta ICJ ta umurci Isra'ila a watan Janairu da ta guji duk wani abu da ka iya fadawa karkashin rukunin kisan kare dangi da kuma tabbatar da cewa sojojinta ba su aikata kisan kare dangi a kan Falasdinawa ba, bayan da Afirka ta Kudu ta zargi Isra'ila da kisan kare dangi a Gaza.

A cikin watan Janairu, Shugaba Tayyip Erdogan ya ce, Turkiyya na ba da takardun shaida a kotun ICJ, wadda aka fi sani da kotun duniya.

Isra'ila da kawayenta na Yamma sun bayyana zargin a matsayin mara tushe. Hukuncin karshe dai kan shari'ar da ICJ ke yi kan karar da Afirka ta Kudu ta shigar a birnin Hague na iya daukar shekaru.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG