Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Tsageran Boko Haram Sun Mamaye Madagali


Wadansu mutane suna kallon barazunan gine gine bayan harin Boko Haram.
Wadansu mutane suna kallon barazunan gine gine bayan harin Boko Haram.

Rahotanni sun ce a yanzu haka ‘yan tsageran Boko Haram sun fara mamaye yankunan Madagali mai makwabtaka da jihar Adamawa.

Kwanaki hudu bayan kwace makarantar horas da zaratan ‘yan sanda dake Limankara a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno, rahotanni sun ce a yanzu haka ‘yan tsageran Boko Haram sun fara mamaye yankunan Madagali mai makwabtaka da jihar Adamawa.

A cikin hirarsu da wakilinmu Ibrahim Abdul’aziz, wadansu mazauna garin Madagali, wanda ke dab da bakin iyakar Borno da Adamawa, kuma mai tazarar kilomita 20 kacal da Gwoza, sun ce sun ga mayakan Boko Haram cikin motoci sun fara kewayewa da mamaye wadansu kauyuka.

Shaidun suka ce, jami’an tsaro kalilan da suke wurin sun arce da isowar mayakan abinda ya tilasa mazauna kauyen suma kaura da neman ceton rayukansu.

Shima a cikin bayaninsa, shugaban karamar hukumar Madagali James Wartadda ya tabbatar da lamarin ya kuma ce jami’an tsaro basu da wani tasiri a wurin.

Ga cikakken rahoton Ibrahim Abdul’aziz.

Kungiyar Boko Haram ta Mamaye Madagali - 2'42"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:42 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG