Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Ne Za’a Rantsad Da Sabon Gwamnan Jihar Kogi


Nigerian President Goodluck Jonathan, left, takes the oath of office before Justice Sunday Olorundanusi, center, and Chief Justice of Nigeria Katsina Alu during his inauguration ceremony at the main parade ground in Nigeria's capital of Abuja Sunday, May
Nigerian President Goodluck Jonathan, left, takes the oath of office before Justice Sunday Olorundanusi, center, and Chief Justice of Nigeria Katsina Alu during his inauguration ceremony at the main parade ground in Nigeria's capital of Abuja Sunday, May

A yau laraba ne za’a rantsad da sabon gwamnan jihar Kogi dake tarayyar Najeriya Alhaji Yahaya Bello

Hukumar zaben Najeriya ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe karashen zaben gwamnan jihar wanda akayi bayan mutuwar dan takaran gwamnan jihar ta Kogi a karkashin tutar jamiyyar APC.

A wani taron manema labarai a jiya talata shugaban kwamitin labarai na bikin rantsuwar Alhaji Ishaq Ajibola yace sun kammala duk wani shiri da ya dace wanda zaisa ayi bikin cikin nasara.

To sai dai ga bisa dukkan alama za a rantsad da gwamnan ne ba tare da mataimaki ba, domin tuni Mr James Faleke yayi watsi da mukamin mataimakin.

Amma akan wannan batun Alhaji Ishaq Ajibola ya bayyana mafita. Inda yake cewa.

‘’Yace ina gani jamiyya ta warware wannan batu ko a jiya shugaban jamiyya ya fada a taron manema labarai cewa jamiyya nada hayar fitar da wani sabon mataimaki’’.

To menene ‘yan jihar ke bukata ga sabon gwamna Yahaya Bello?

Ga Mustafa Nasir Batsari da Karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:40 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG