Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zaben Ghana: Shugaban Zango Ya Musanta Shirin Ta Da Rikici


Allunan tallata manyan 'yan takara a zaben kasar Ghana da za a yi a mako mai zuwa
Allunan tallata manyan 'yan takara a zaben kasar Ghana da za a yi a mako mai zuwa

Cikin 'yan kwanaki kalilan ne al'umar kasar Ghana za ta garzaya zuwa rumfunan zabe, domin kada kuri'u a zaben shugaban kasar.

Shugaba mai ci John Dramani Mahama zai yi takara ne tare da fitattun 'yan siyasa irinsu Nana Akufo-Ado na jam'iyar New Patriotic Party da Ivor Greenstreet na jam'iyar Convention People's party da sauran su.

A shirye-shiryen zaben na Ghana an jima ana rade-radin barkewar rikici a lokacin zabe, koda yake hukumomin sun musanta hakan tare da ba da tabbacin cewa za a dauki matakan tsaron.

Daga irin rahotannin da ake samu akwai cewa al'umar yankin Zango, wadanda mafi yawansu Hausawa ne, za a yi amfani da su wajen ta da tarzoma.

Amma a wata hira da abokin aikinmu na sashen Ingilishi Peter Clottey ya yi da shugaban mutanen Zango, Alhaji Baba Isah, ya musanta wannan batu na shirin ta da tarzoma:

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:17 0:00

XS
SM
MD
LG