A daidai lokacin da duniya ke komawa fannin amfani da iskar gas don rage illolin sauyin yanayi ga al’umma, gwamnatin Najeriya ta kaddamar da muhimman ayyukan samar da iskar gas guda uku a jihohin Imo da Delta.
Shugaban Hukumar bada agajin gaggawa na jihar Yobe wato YOSEMA, Dakta Mohammed Goje ne ya bayyana hakan a yayın hira ta musamman ga Muryar Amurka.
Kungiyoyin fararren hula da masana shari’a a Najeeriya sun fara jan hankalin gwamnati cewa kada ta yarda a yi tsarin sasantawa a wajen kotu ko kuma "Plea Bargain" a turanc, wato ba da wani kason kudin da ake zargi don a rufe batun.
An gurfanar da Hadi Sirika ne a gaban Mai Shari’a Sylvanus Oriji na babbar kotun tarayya da ke zamanta a birnin Abuja tare da diyarsa, Fatima, da surkinsa, Jalal Sule Hamma, da wani kamfani mai suna Al Buraq Global Investment Limited.
'Yan Najeriya daga sassan kasar daban-daban ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyinsu da nuna shakku da rashin fahimtar yadda tsarin yake, jim kadan bayan fitowar sanarwar bankin CBN wanda za’a fara aiwatarwa nan da makwanni biyu daga ranar da sakon ya fito.
Batun rage farashin wutar lantarki a Najeriya dai na ci gaba da jawo muhawara mai karfi ne tun bayan fito da sanarwa da kamfanin rarraba wutan lantarki na Legas wato Ikeja Electric ya yi a ranar Litinin.
A daidai lokacin da karanci da tsadar man fetur ke kara kamari a kusan dukkan sassan Najeriya, an sami sabani da ka iya tsananta matsalar tsakanin bangarorin da lamarin ya shafa, kamar kungiyar ciyamonin depot-depot na IPMAN, kamfanin NNPCL da ma hukumar NMDPRA.
Jim kadan bayan kamalla wani babban taro na musamman a kan yaki da ayyukan ta’adanci a nahiyar Afrika, kasashen nahiyar baki daya sun ce sun shirya tsaf don fitar da sabbin dabarun bai daya na yaki da matsalolin tsaro a matakin shiyya, tare da goyon bayan wasu kungiyoyin kasashen Turai kamar EU.
A yayin da ake ci gaba da lalubo hanyoyin kawo karshen matsaloli masu alaka da ayyukan ta’adanci a Najeriya, ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara a harkokin tsaro da Majalisar Dinkin Duniya da wasu kasashen Afrika sun hada kai wajen neman mafitar kalubalen tsaro da suka addabi kasashen Afrika.
A yayin da alkaluma suka yi nuni da cewa wasu kamfanonin jiragen saman waje sun shiga takun saka da kamfanin Airpeace, hukumar kula da kungiyoyin fararen hula ta Najeriya NCSCN da wasu masana tattalin arziki sun bukaci gwamnati ta tallafawa kamfanin na cikin gida.
Masu kamfanonin shirya tafiye-tafiye na ta bayyana yakinin cewa akwai yiyuwar farashin tikitin kamfanin airpeace ya yi tasirin kawo sauki a saura kamfanonin tafiye-tafiyen kasashen waje da suke takurawa ‘yan kasar nan da muguwar tsada bada jimawa.
A daidai lokacin da wasu ‘yan Najeriya ke korafe-korafe a kan kayyade yawan kudin da zasu rika cira a ATM ko kuma a cikin banki da ake kallo a matsayin yiwuwa akwai karancin takardun kudi ne a kasar, masu ruwa da tsaki a fannin hada-hadar kudi a bankuna sun ce babu matsalar karancin kudi.
Wannan matakin dai na nufin cewa sabon kudin ruwan ya tashi ne daga kaso 22.75 bisa dari da kwamitin MPC ya sanar kusan wata daya da ya gabata da kuma karin shi ne karo na biyu da kwamitin karkashin jagorancin gwamnan Babban Bankin, Olayemi Cardoso ke dauka.
Dan siyasar Uganda, Kyangulanyi wanda aka fi sani da Bobi Wine ya ce zaben fim dinsa, The People’s President domin takarar lambar yabo, ya taimaka wajen janyo hankalin duniya kan gwagwarmayar da yake yi ta samar da sauyin dimokaradiyya a kasarsa.
Rahotannin dake fitowa daga fadar gwamnatin jihar Kaduna sun yi nuni da cewa an sako gomman dalibai da aka sace daga garin Kuriga na jihar Kaduna.
A yayın da ake bukin Ranar Mata ta Duniya a yau Juma’a 8 ga watan Maris na shekarar 2024, wanda aka yiwa taken Zuba jari ga mata: Habaka ci gaba, dubban mata na jan hankali a kan yiyuwar jefa Mata miliyan 340 a duniya cikin tsananin talauci idan ba’a dauki matakan da suka dace cikin gaggawa ba.
A yayin da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da kama wasu mutane 15 da ake zargi da wawure wani rumbun adana kayayyakin abinci a unguwar Karmo da ke Abuja, masana tattalin arziki da tsaro sun ce gwamnati ta san abun da ya kamata ta yi.
Ba za a sami nasarar hade layikan salula da lambar Shaidar Dan Kasa ba idan ana amfani da karfin iko a maimakon bin mutane da lalama a cewar masana.
Kasa da kwana 2 da rufe layikan sadarwa al’ummar Najeriya na kokawa a kan yadda wannan matakin ke ci gaba da jawo musu asara kuma wasu masana ke cewa a cikin lallami ya kamata a bi yan kasa don hade layukansu da lambar shedar dan kasa, wasu kuma na ganin dole a Fifita ‘yancin ‘yan kasa a kan komai.
Domin Kari