Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An sami Asarar Rayuka A Tarzoma Da Aka Yi A Birnin Niamey


Zanga zanga a Jamhuriyar Nijar
Zanga zanga a Jamhuriyar Nijar

Wata majiya da ba ta gwamnati ba ta tabbatar da mutuwar mutane kimanin uku a zanga zangar da aka gudanar a birnin Niaamey fadar gwamnatin Jamhuriyar Nijar, biyo bayan mummunar tarzoma da aka yi da aka kona majami’u da dama da kuma wadansu cibiyoyin gwamnati.

Masu zanga zangar dai suna nuna fushinsu ne dangane da zanen batancin da aka yiwa annabi Muhammadu SWA da mujallar barkwancin nan ta kasar Faransa Charlie Hebdo tayi, bayan harin ta’addancin da aka kai mata da aka kashe ma’aikatanta goma sha biyu.

A cikin hirarshi da Sashen Hausa wani malamin makaranta da aka yi abin a ganin idonsa, Issoufou Mamane Moutari ya bayyana cewa, hukumomi sun kama Limaman Musulmi da dama dangane da tashin hankalin kafin daga baya aka sakesu.

Bisa ga cewarshi an kona majami’un kirista da dama yayin tarzomar. Ya kuma ce I zuwa lokacin hira da Sashen Hausa ,kura ta fara lafawa, yayinda kuma aka girke jami’an tsaro a muhimman wurare, duk da haka yace ana zama zullumi, da gudun kada lamarin ya sake aukuwa.

Ga cikakkiyar hirar.

Rahoton Zanga Zanga a Miamey
please wait

No media source currently available

0:00 0:05:12 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG