Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Na Goyon Bayan Karfafawa Korea ta Arewa Takunkumi


Roka da Korea ta Arewa ta harba.12-12-12
Roka da Korea ta Arewa ta harba.12-12-12
Jakadun kasa da kasa a Majalisar Dinkin Duniya sun bayyana ra’ayin goyon bayan bai daya game da batun samun daidaituwa tsakanin Amurka da China domin karfafa takunkumi a kan Korea ta Arewa saboda gwajin rokan da tayi a watan Disamban da ya gabata.

Jakadun kasa da kasa a Majalisar Dinkin Duniya sun bayyana matsayinsu ne a takardun bayanan daftarin kudurin da suka rika rarrabawa ga wakilai goma sha biyar na kwamatin sulhu da tsaro a Majalisar Dinkin Duniya, ana kyautata cewar wani lokaci a yau Talata ce kwamatin zai yi muhawara sannan a jefa kuri’ar amincewa horas da Korea ta Arewa kan batun harba rokokin da tayi.
XS
SM
MD
LG