Tagwayen fashewar bam din mota a yankin Tuddan Golan, bangaren rikon ya yi sanadiyar mutuwar mutane 8 yau jumma’a yayinda dakarun gwamnatin suka kaddamar da sabon samame a yankin Damascus da yan tawaye suka kwace.
Kungiyar kare hakkin yan adam ta Syria ta Observatory ta ce yawancin wadanda suka mutu a fashewar bam din na Golan sojojin leken asiri na Syria ne.
Har Yanzu ba a sami wanda ya dauki alhakin harin ba , duk da cewar sanya bam da harin kunar bakin wake wata dabara ce da mayakan ‘yan kishin islama ke amfani da ita suna yakar dakarun Syria, a yayinda su da ‘yan tawayen ke kokarin hambare shugaba Bashr al-Assad.
Kungiyar kare hakkin yan adam ta Syria ta Observatory ta ce yawancin wadanda suka mutu a fashewar bam din na Golan sojojin leken asiri na Syria ne.
Har Yanzu ba a sami wanda ya dauki alhakin harin ba , duk da cewar sanya bam da harin kunar bakin wake wata dabara ce da mayakan ‘yan kishin islama ke amfani da ita suna yakar dakarun Syria, a yayinda su da ‘yan tawayen ke kokarin hambare shugaba Bashr al-Assad.