Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Binciken cin hanci da rashawa a Najeriya yanzu aka fara - Buhari


Shugaba Muhammad Buhari na Najeriya
Shugaba Muhammad Buhari na Najeriya

Yayinda yake ganawa da 'yan Najeriya mazauna Abu Dhabi a Hadaddiyar Daular Larabawa shugaba Buhari yace sunayen wadanda ba'a bayyana nan gaba sun fi na baya. Akan Boko Haram kuma yace gwamnati ta karya lagonsu.

A jawabin da ya yiwa 'yan Najeriya dake Hadaddiyar Daular Larabawa yace gwamnatinsa tayi gagarumar nasara wajen karya lagon kungiyar ta'adancin nan ta Boko Haram.

Nan ba dadewa ba shugaban yace zasu tunkari tsagerun 'yan yankin Neja Delta dake tda hankalin al'umma saboda sun shahara wajen fashe bututun man fetur suna satar mai na kuma sace mutane.

Akan yaki da cin hanci da rashawa shugaban yace daga yanzu za'a kara jin sunayen manyan mutane da suka wawure kudaden Najeriya.

Akan wannan bayani ne Daular Larabawan tace zata taimaka ta ga an kwato kadarorin kasa rtare da tasa keyar nutanen zuwa Nageriya domin a hukuntar dasu.

Ga karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG