A daidai lokacin da wasu ‘yan Najeriya ke korafe-korafe a kan kayyade yawan kudin da zasu rika cira a ATM ko kuma a cikin banki da ake kallo a matsayin yiwuwa akwai karancin takardun kudi ne a kasar, masu ruwa da tsaki a fannin hada-hadar kudi a bankuna sun ce babu matsalar karancin kudi.
Shugaban kamfanin Binance dake tsare a hannun hukumomin Najeriya, Tigran Gambaryan ya maka Mashawarcin Shugaban Kasa Akan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu da Hukumar EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa a kotu bisa zarginsu da tauye masa hakkokinsa na bil adama.
Tun dai bayan dawowar daliban Kuriga da na jihar Sakkwato da ‘yan bindiga suka sace domin karbar kudin fansa, ake ta samun ra'ayoyi mabambanta dangane da yadda aka ceto daliban.
Najeriya za ta ba da sabbin lasisin hakar ma'adinai ne kawai ga kamfanonin da suka gabatar da wani shiri kan yadda za a sarrafa ma'adanai a cikin gida, karkashin sabbin ka'idoji da ake samar da su, kamar yadda kakakin gwamnati ya tabbatar a ranar Alhamis.
Hedikwatar tsaro ta Najeriya ta bayyana wasu mutane 8 da ake nema ruwa a jallo kan kashe jami’an soji a yankin Okuama da ke jihar Delta.
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya karama zaratan dakarun Rundunar Sojojin Najeriya da wadansu batagari dake kauyen bakin teku suka yiwa kisan gilla da lambar girmamawa na kasa.
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya gana da shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu a fadar aso Villa dake birnin Abuja inda suka tattauna karuwar hare-haren ‘yan bindiga da wasu nau’ukan ta’adanci a jiharsa.
Masana tsaro da sauran jama'a a Najeriya na ci gaba da tsokaci tare da nuna jin dadi, a kan labarin mutuwar kasurgumin ‘dan bindigan nan Dogo Gide da aka tabbatar da mutuwar sa a jihar Sokoto.
Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana amincewar gwamnatinsa na rage wa maniyyatan hajjin bana naira dubu 500 bayan da Hukumar Alhazan Najeriya ta kara naira miliyan 1.9 akan kudin hajjin bana.
Wannan matakin dai na nufin cewa sabon kudin ruwan ya tashi ne daga kaso 22.75 bisa dari da kwamitin MPC ya sanar kusan wata daya da ya gabata da kuma karin shi ne karo na biyu da kwamitin karkashin jagorancin gwamnan Babban Bankin, Olayemi Cardoso ke dauka.
Wata babbar kotu da take Kano a Najeriya ta yankewa ‘dan China Frank Geng-Quangrong da ya kashe Ummulkhulsu Buhari har lahira a shekara 2022 hukuncin kisa ta hanyar rataya
Mawallafin Desert Heral da ke Kaduna, Tukur Mohammed Mamu, ya yi barazanar maka babban lauyan gwamnatin tarayyar Najeriya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), a kotu saboda ayyana shi a jerin masu daukan nauyin ta’addanci a kasar.
Domin Kari
No media source currently available