A shekara ta 2022 ne shugaban bankin raya musulinci wato IDB, Dr Muhammad Al-Jasser ya kaddamar da shirin bankin na raya noma da kiwo a jihar Kano da nufin samar da abinci da dakile rikici tsakanin manoma da makiyaya
Mataimakin kwamandan hukumar Hisbah Dr. Mujahidin Aminuddin Abubakar ya yi kira ga iyaye da su sa ido sosai kan harkokin ‘ya’yansu.
A watan daya gabata, IPMAN tayi barazanar durkusar da harkar samarda man fetur a Najeriya, akan rashin biyan bashin Naira biliyan 200 ta kudaden dakon man.
Lauyan Hukumar EFCC, mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati, Oluwaleke Atolagbe, ya shaidawa alkalin kotun, Mai Shari’a Suleiman Belgore, cewar ba’a mikawa tsohon ministan da kaninsa sammacin dake kunshe da tuhumar a cikinsa ba.
Wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da mutane 105 a yankin Arewa maso yammacin Najeriya a makon da ya gabata, ba kudin fansa su ke so ba, tattaunawa su ke so da gwamnatin jihar Zamfara, kamar yadda wasu iyalai biyar suka shaida bayan da ‘yan bindigar suka tuntube su a ranar Litinin.
‘Yan Najeriya daga shiyoyin kasar kama daga Kano, Filato, Bauchi, Kaduna, Neja da dai sauransu sun ce lallai kungiyoyin sun rufe ofisoshin DisCos amma ba su ga wani tasiri da zanga-zangar ya yi a kasar ba.
Shugaban Hukumar bada agajin gaggawa na jihar Yobe wato YOSEMA, Dakta Mohammed Goje ne ya bayyana hakan a yayın hira ta musamman ga Muryar Amurka.
Wata majiyar soji ta bayyana cewar an samu nasarar kubutar da mutanen ne sakamakon samun wani kiran gaggawa a ranar 11 ga watan Mayun da muke ciki, da misalin karfe 12 rana.
Shigar da karar ya biyo bayan faifan bidiyon daya karade shafukan sada zumunda a ‘yan makonnin da suka gabata inda aka wasu dalibai suna cin zalin Namitra Bwala.
Matakin ma’aikatan na zuwa ne biyo bayan umarnin hadin gwiwa da kungiyar kwadago ta Nlc da takwararta ta Tuc suka baiwa mambobinsu a karshen mako na cewa su kargame ofisoshin domin nuna adawa da karin kudin wuta.
A ranar Alhamis wasu ‘yan bindiga suka kutsa jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara a jihar Kogi suka kwashi dalibai da dama suka yi cikin daji da su.
Shugaba Bola Tinubu ya bukaci Babban Bankin Najeriya da ya dakatar da aiwatar da dokar haraji ta yanar gizo da ya dora kan 'yan kasa wacce aka fi sani da cybersecurity levy, sannan ya bayar da umurnin a sake nazarin matakin.
Domin Kari
No media source currently available
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa
Hukumomi a Najeriya sun daura damarar yaki da magudin zabe, a wani muhimmin lamari ga dimukradiyya a Afirka. Bayan babban zaben 2023, Najeriya ta fara daukan matakan hukunta wadanda aka samu da laifin magudin zabe domin dawo da martabar tsarin zabe a kasar.
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.