Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Henri Konan Bedie Ya Bayyana Goyon Baya Ga Alassane Ouattara


Magoya bayan shugaba Laurent Gbagbo su na kallon yadda ake bayyana sakamakon zabe a Abidjan
Magoya bayan shugaba Laurent Gbagbo su na kallon yadda ake bayyana sakamakon zabe a Abidjan

Tsohon Firayim ministan ya samu wannan goyon bayan da aka ce yana da matukar muhimmanci a zagaye na biyu na zaben shugaban kasa

Tsohon Firayim ministan kasar Ivory Coast ya samu goyon bayan da ka iya zamowa mai matukar muhimmanci a zaben fitar da gwani na shugaban kasa da zai kara da shugaba Laurent Gbagbo nan gaba cikin watan nan.

Jiya lahadi, tsohon shugaba Henri Konan Bedie yayi kira ga magoya bayansa da su jefa kuri’unsu ma Alassane Ouattara a zaben fitar da gwanin na ranar 21 ga watan nan na Nuwamba. Mr. Bedie shi ya zo na uku a zagayen farko na zaben shugaban kasar da aka ranar lahadi ta sama, inda ya samu kashi 25 cikin 100 na kuri’un da aka jefa.

Ma'ikatan zabe na Ivory Coast su na kidaya kuri'u lokacin zagayen farko na zaben shugaban kasa ranar Lahadi 31 Oktoba 2010
Ma'ikatan zabe na Ivory Coast su na kidaya kuri'u lokacin zagayen farko na zaben shugaban kasa ranar Lahadi 31 Oktoba 2010

Shugaba Gbagbo, wanda ya samu kashi 38 cikin 100, da Ouattara, wanda ya samu kashi 32 cikin 100, sun haye za su gwabza a zagaye na biyun. Tun kafin wannan zaben, Mr. Bedie da Mr. Ouattara sun yi alkawarin zasu goyi bayan kowane daya daga cikinsu idan ya haye zai fuskanci shugaba Gbagbo a zagaye na biyu.

Zaben da aka yi a ranar lahadi ta sama shi ne zaben shugaban kasa na farko tun yakin basasar shekarar 2002.

Wa’adin shugaba Gbagbo a kan mulki ya kare tun shekarar 2005, amma an sha jinkirta gudanar da zabe a saboda kasa karbe makaman ‘yan tawaye da kuma gardama a kan wadanda suka cancanci jefa kuri’a a kasar.

XS
SM
MD
LG